Wednesday, October 8, 2008

Azumin Sittu Shawwal

Azumin Sittu Shawwal

Imamu Muslim ya fitar da Hadisi ingantacce Daga Abu Ayyub Al'ansari Allah Yakara Yarda agareshi daga ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace: (Duk Wanda ya Azumci Ramadan Sannan Y bishi da Azumi Shida a cikin Shawwal ya kasance kamar wanda ya Azumci shekara) Muslim.

Azumin kwana shida na watan sallah wato watan shawwal kenan Mustahabbine, wannan shine zancen mafiya yawa daga cikin malamai, wasu kuma sukace makaruhi ne saboda jin tsoron kada a dauka cewa shima wajibi ne kamar na Ramadan.

Yadda Ake Azumtansa

Malamai sunyi zantuka guda uku (3) kamar haka:

1. Yin Azumin guda shida ajare a farkon watan.

2. Yin Azumin ajere ko a rarrabe duka daya ne a kowani lokaci a cikin wata.

Fa'idan Azumin Shawwal

1. Yin Azumi Shida na Shawwal yana Cika ladan Azumin shekara.

2. Azumin Shawwal kamar Sallolin Nafiloli ne da'ake yi kafin da bayan Sallaolin farilla. Wanda suke cika nak'asa da tasamesu

Tuesday, September 23, 2008

I'ITIKAFI

I'ITIKAFI

Dasunan Allah mai Rahama Mai Jinkai

Shine lazimtan masallaci da zama cikinsa da niyyan samun kusanci zuwa ga Allah. kuma malamai sunyi ittifak'I -wato sun hadu- akan cewa itikafi an shar'antashi kuma mustahabbi ne.

Tunatarwa: wasu mutane na kuskure ta yanda suke daukan cewa Itikafi, yakebanci manzan Allah ne Sallalahu Alaihi Wasallam shi kadai, wasu kuma suce hadisin Itikafi an shafe shi, wasu kuma suna dauka cewa Itikafi na dattawane ko akasin hakan, to duk wadannan kurakurai ne ba'a sha. Nana A'isha Allah yakara yarda agareta tace: (Lallai manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yanayin Itikafi a cikin goma na K'arshe na Ramadan har Allah yadauki ransa, sannan matansa sukayi Itikafi a bayansa) Bukhari. Ibn Hjar yace (Ba'a shafe hadisin ba kuma baya cikin abubuwan da suka kebanci ManzanAllah Sallallahu Alaihi Wasallam)fathul baari 4/272.

HUKUNCIN ITIKAFI

Mafi yawan malamai sun tafi akan cewa mustahabbi ne.

Imamu Malik Yace: (Nayi tunani akan al'amarin Itikafi, da abinda yazo akansa, da yanda musulmai suka barshi, tareda cewa manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, be kasance yabarshi ba, se naga cewa sun barshi ne saboda yanada wahala akansu.)

Imam Azzuhri Yace: (akwai mamaki a Al'amarin musulmi! Sun bar Itikafi, tareda cewa Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, be barshi ba tunda yazo Madinah , har Allah madaukakin Sarki yadauka ransa.)

SHARUDDAN ITIKAFI

1. MUSULUNCI: baya inganta ga wanda ba musulmi ba.

2. HANKALI: mahaukaci baya itikafi, saboda koda ibada ta wajibi bata zama dole akansu ba, andaga alkalami akansu.

3. NIYYA: sharad'I ce ga dukkan ibadodi, kuma duk aikmin da babu niyya a cikinsa ba karbabbe bane.

4. MASALLACI: ga namiji dolene yayi a masallaci, amma mace kuma anyi sabani akanta, Malam SUHNUNU Yace: (nace ma ibnul K'asim: menene zancen Imamu Malik gameda Itikafin mace tayi amasallacin jama'a? se yace Na'am, yace: a zancen Malik tayi Itikafi a masallacin gidanta? Se yace: Hakan baya burgeni, ana itikafi ne a masallacin da'aka yishi dan Allah.) Mudawwana 1/295.

Sheikh Aminul Hajj yace: (amma yafi rinjayen dalili awurina shine mace tayi Itikafinta a gidanta, wato wurin da takebance shi tana sallah a cikinsa.

5. AZUMI: wasu daga cikin malamai sukace kada mutum yayi itikafi face yaname Azumi, an tambayi Ibnul K'asim: (shin anayin itikafi batare da azumi ba a cikin zancen Malik? Se yace: ba'ayi se da Azumi. Wasu kuma sukace anayi koda mutum beyi Azumi ba, Sukace wannan shine ra'ayi mafi rinjayen dalili, saboda Hadisi Umar ingantacce da Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya Umarce shi da yayi itikafi yayin da yace masa yayi alwashin yin hakan a jahiliyya, kuma be ce masa yayi Azumi ba.

6. IZINI: dolene se miji yayi wa matarsa izini ko abinda ya mallaka na bawa ko baiwa, miji mace yana gida ne ko yayi tafiya dole tanemi izininsa, kuma idan yayi mata izini, to be kamata ya hanata ba kuma.

RUKUNNAN ITIKAFI

1. Zama a cikin Masallaci. 2. Nisantan Jima'I da abubuwan da zasu iya kaishi yin hakan. 3. Nisantar manyan laifuka. 4. Musulunci. 5. Hankali. 6. Tsarki daga Haila. Itikafi yana baci saboda rashin daya daga cikin wadannan.

ABUBUWAN DASUKE BATA ITIKAFI

1. FITA DAGA MASALLACI: baya halasta fita daga masallaci, In banda fita saboda: dan Biyan bukata kamar fitsari ko bayan gari, wankan janaba da na jumu'ah, cin abinci ko abin sha idan be iya ci ko sha a wurin da yake itikafi, idan yaji tsoron wuta ko sata kom rushewan gini, in aka fitar da shi da karfi, idan mace tayi haila da sharadin ta dawo da tayi tsarki, idan mijin mace yarasu ko yasake ta zata fita a mafi rinjayen zancen malamai biyu wasu sukace zata cigaba har seta kammala, fita saboda yin Umara, fita da mantuwa, idan yayi hauka ko suma.

2. YIN JIMA'I: saboda Allah yace: (kuma kada ku sadu dasu, alhalin kuna masu Itikafi a cikin masallatai…) Sur.Baqarah-186. haka sun bantan mace da sha'awa.

3. YIN RIDDA:wato fita daga musulunci

4. YIN MANYAN LAIFUKA: kamar yin zina da sata acikin itikafi, wanda mutane suna sakaci da daukan abin wani ko da kadan kuwa se a kiyaye.

5. YIN HAUKA KO SUMA: yana bata itikafi se dai idan yasami lafiya ko ya farfad'o to se yacigaba.

6. HAILA: idan mace tayi haila itikafinta ya baci, amma idan tayi tsarki se ta cigaba, na bayan be baciba.

ABUBUWAN DA BA'ASO GAME ITIKAFI

Ba'aso me itikafi ya shagaltu da abinda ba ambaton Allah ba, da kuma abinda ba dolene ba.

1. jayayya. 2. zagi damaganganun banza. 3. Yin giiba da Annamimanci. 4. Kallon abinda yake haramun. 5. Rashin yin magana gaba daya tun daga safe har dare da sunan bauta.

Tunatarwa: wasu daga cikin daliban ilimi se kaga suna zuwa itikafi da wasu littafai na karatunsu suna yin muraja'a, ba haramun bane amma kamata yayi tunda kwanakine yan kadan a cikin shekara, meze sa bazakayi hakuriba, sauran kwanakin shekara kayi acikinsu.

ABUBUWAN DASUKA HALASTA GAME ITIKAFI

1. Yin wanka da canza kaya, da sanya kayan da yakeso.

2. Cin Abinci da Shan Abin Sha a cikin masallaci.

3. Yin magan da yan uwa, amma ba'ason yawaita surutu da mutane.

4.Ya nemi Aure ko a daura masa Aure.

5. Yin Aski da yanke Farce.

6. Sanya turare.

ABUBUWAN DA SUKE MUSTAHABBI GA ME ITIKAFI

1. Mustahabbi ne ga me itikafi, yakafa tanti da ze kangeshi daga jama'a, inbe samu ba se ya lazimce wurin da babu jama'a ta yanda baze barshi ba seda larura.

2. kiyaye yin Sallah cikin jama'a, da nafiloli.

3. Yawan karatun alk'ur'ani, da rashin shagaltuwa da abinda ba ruwa.

4. Yawan ambaton Allah, zikiri, da tasbihi.

5. Yin azumi a cikin wantan da ba ramadan, ga wanda zeyi itikafi da rana.

6. Yawan yin kokari wajen d'a'a.

MAFI KARANCIN ITIKAFI DA MAFI YAWANSA

Itikafin neman lada baya da kad'an ko mafi yawa, se dai wanda yayi Itikafi a goman k'arshe na Azumin kada ya fita se idan anga watan Sallah wato Shawwal, malamai sun hadu akan cewa baya da mafi yawa, amma sunyi maganganu akan karancinsa, wasu sukace mafi karancinsa Sa'a, wasu sukace Yini daya da dare, wasu sukace kwana goma.

Imamul k'urtabi yace: ( mafi karancin itikafi a wajen Malik, da Abu Hanifa, dare da yini….)

YAUSHE AKE SHIGA ITIKAFI KUMA YAUSHE AKE FITA

A. Shiga wajen itikafi:akwai zancen malamai guda biyu:

1. Shiga bayan sallar Asubahin ranar Ashirin da d'aya na Ramadan, saboda hadisin Nana A'isha Allah yakara mata yarda tace: (Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam idan ze shiga itikafi yana yin sallar Asubahi, sannan se yashiga wurin itikafinsa) Bukhari. kuma wannan shine mafi rinjayen dalili. Kuma mazhabinAhmad da Laith da Ishak'.

2. Shiga kafin rana r daren Ashirin da d'aya ta fad'i, wannan shine mazhabin Malamai hud'u

B. Fita daga itikafi: Ana fita daga wurin itikafi bayan ganin watan sallah, wasu kuma sukace mustahabbine ya bari har yayi sallar idi sannan ya tafi.

SIRRIN DA YAKE CIKIN I'ITIKAFI

Bauta tana da sirruka da hikimomi masu yawa, saboda ayyuka gaba daya, makewayansu itace Zuciya, kamar yanda Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam Yace (..Kusaurara! lallai acikin jiki akwai wata tsoka wanda idan ta gyaru, to dukkan sauran jiki ya gyaru, kuma idan ta bace, to dukkan Sauran jiki ya baci, ku saurara! Itace zuciya.) Bukhari da Muslim.

To in muka duba zamuga cewa mafi yawan abubuwan da suke bata zuciya, sune sha'awan cin abinci da abin sha da saduwa da Iyali da Zancen da ba na dole ba, da barcin da ba na dole ba, da abokai da basu da wata fa'ida da sauran abubuwa dasuke kawar da zuciya daga yin abinda yake biyayya ne ga Allah, se Allah ya Shar'anta wasu abubuwa na lada da zasukare zuciya daga rud'ani da shagaltuwa daga ambaton Allah, kamar Azumi wanda yake hana mutum cin abinci da abin Sha da Saduwa da Iyali da rana. To wannan hanuwan daga wadannan abubuwan jin dadi, shine yake karfafa alak'a tsakanin mutum da Ubangijinsa, da fuskantar dashi ga Lahira, kena Azumi garkuwa ce datake kare zuciya daga abubuwan sha'awa da suke kawar da mutum daga yin biyayya ga Allah, duk da hanine wanda yake matsakaici saboda an halasta wa mutum wadannan abubuwa a cikin dare.

To haka shima Itikafi yanada Sirri me girma, shine Kare mutum daga yawan cakud'a da jama'a, da yawan magana, saboda me Itikafi yana shagaltuwane da karatun Alk'ur'ani da Tsayuwa –wato yin sallah- da Zikiri da yawan yin Addu'a da makamantansu, haka kuma akwai kariya daga yawan barci, tunda yazo ibada ne ba barci ba, to wadannan abubuwa barinsu shike kara sa zuciya ta fuskanci Allah.

ABUBUWAN TUNATARWA

* Wasu daga cikin malamai sun tafi akan cewa ba'ayin Itikafi se a masallatai guda Uku kamar yadda yazo a cikin Hadisi, na hani akan yin Itikafi a masallatan da basuba, manzan Allah Sallalahu Alaihi Waasallam yace (Babu Itikafi face a masallatai guda uku) imamu Tahawi. -Wato masallacin Harami wato Ka'abah da masallacin Madinah da masallacin Aqsa wato Kudus-, Malamai suka fassara shi da cewa hani ne na yin alwashin yin Itikafi a wani masallaci da tafiya zuwa gareshi saboda hakan se a wadannan masallatan kadai ya halatta, ayi hakan saboda duk malaman mazhabobi Hud'u sun hadu akan cewa ya halatta ayi a kowani masallacin Juma'a.

* wasu sukan bar ayyukansu na wajibi saboda suyi Itikafi, to yin hakan kuskure ne saboda shi Itikafi sunna ce, saboda haka ba'a barin abinda yake wajibi saboda Sunnah.

Ya Allah Ka Karba mana dukkan Ayyukanmu a cikin Watan Ramadana kasa Muna cikin Bayinka Yantattu dag Wuta kuma kadatarmu da daren Lailatul K'adari. Amiin

Wata Me Tarihi

Yin Bushara da Azumin Ramadan

Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya kasance yana yima Sahabbansa Bushara da shifa watan Ramadankamar yadda Imamu Ahmad da Imamu Nasa'I suka kawo Hadisin da Abu Hurairah ya ruwaito daga Manzan Allah Sallalahu Alaihi Wasallam yace manzan Allah yakasance yanayiwa Sahabbansa Bushara "Hak'ik'a watan Ramadana mai albarka yazo maku, Allah ya wajabta maku Azumtansa, Ana bud'e kofofin Aljanna acikinsa kuma ana kulle kofofin Wuta , kuma ana D'aure Shaidanu acikinsa, akwai dare da tafi wata dubu acikinsa…………"

Watan Ramadan Yanada Wadansu Falala:

1. Watan da'aka Saukarda Alk'ur'ani 2. watan Taraawih da Tahajjud. 3. Watan Tuba da Kankare Zunubai. 4. watan Daure Shaid'anu. 5. watan da'ake kulle kofofin Wuta. 6. watan da'ake bud'e kofofin Aljanna. 7. watan kyauta da Ihsani. 8. watan da'ake y'antawa daga wuta. 9. watan Lailatul K'adr. 10. watajnAddu'a. 11. watan Jihadi. 12. watan da'ake nunka Lada acikinsa. 13. watan Hak'uri da Godiya.

Wata Me Tarihi

Watan Ramadan Watane me Tarihi acikin Musulunci wanda acikinsa aka Samu da yawa daga cikin Nasarorin yak'i da Kafirai. Gasu kamar haka:

Shekar Ta Farko: acikin Ramadan aka aika Sariyya ta farko k'ark'ashin jagorancin Hamza bn Abdulmutallib, se Sariyyan Ubaidah binil Harith, domin sanya tsoro acikin zukatan Kafirai.

Shekar Ta Biyu: acikin Sha bakwai ga Ramadan akayi Yak'in Badar Alkubra.

Shekar Ta Uku: a cikin Ramadan manzan Allah Sallahu Alaihi Wasallam ya Shirya Runduna a madinah domin su hana mushrikai dasuke son daukan Fansan Yak'in Badr.

Shekar Ta Biyar: Shiryawa Yak'in Khandaq, anyi yak'in ne acikin watan Shawwal wato watan Sallah kamar yanda Imamu bnil Qayyim yace Sun shirya mashi da wata d'aya wato suna hakk'a ganuwa.

Shekar Ta Shida: Sariyyan Gaalib bin Abdullah wanda ta kunshi mutum da'ri da talatin wanda sukayi nasara akan bani Abdullahi bn tha'alabah.

Shekar Ta Takwas: Bud'e Makkah acikin Ashirin ga Ramadan Allah ya daukaka Addininsa da manzansa da muminaikuma ya tseratar da Dakinsa me alfarma daga Hannun Mushrikan K'uraishawa, manzan Allah Sallalalhu Alaihi Wasallalm ya Shigeta tare dashi akwai Sojojin Musulunci dubu Goma.

Shekar Ta Tara: Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam shi da Sahabbaqnsa suka dawo daga Ykin Tabuka.

Shekar Ta Sha Uku: Yak'in Buwaib yakasance cikin ramadan a wuri da ake kira Buwaib kusa da kufa a yau acikin k'asar Iraq inda Farisawa karkashin jagorancin Mahran da musulmai Karkashin Jagorancin Almuthanna bin Harithah wanda yaki me matikar muni ya afku daga karshe Allah yaba musulmai nasara, an kashe da dama daga cikin musulmi, sukuma Farisawa tsakanin wanda aka kashe da wanda suka fad'a cikin ruwan Furat wajen gudu kimanin Dubu D'ari kuma aka samu Ganima me yawa, daganan ne aka karya Lagwan Farisawa. Sannan se Bud'e Garin Nuuba, a kudancin masarkarkashin Jagorancin Abdullahi bin Sa'ad bin Abi Sarah, wandA hakan ya bud'e kofa ga muslunci wajen Yad'uwa a garuruwa da yawa.

Shekar Ta 53: Bud'e TsibirinRuuds, a karkashin Junadah bn Abi Umaiyah.

Shekar Ta 67: Aka Gusar da daular Mukhtar Athak'afi wanda aka kashe a sha hud'u ga ramadan karkashin jagorancin Gwamnan Basra Mus'ab bini Zubair.

Shekar Ta 91: Bud'e Andalus a hannun D'arik' bin Yazid bawan Musa dan Nusair sannan se Yak'in D'urif, musa bin Nusair ya aika wani mutum daga cikin K'abilar Bar-Bar ana kiransa D'uraif da mutane dari hudu da dawakai dari, inda suka tafi suka kai farmaki a gefen tekun Andalus kuma suka dawo da nasara.

Shekar Ta 102: Musulmai suka bud'e Faransa bayan sun kafu a Andalus wato Spain kenan, se suka fara yakan Arewaci da yak'I abayan duwatsun pranis wanda suke tsakaninn Andalus da Faransa wanda da yawa daga cikin dakaru suka jagoranta. Acikin dan wannan gajeren lokaci baze yiwu mu iya ambatan duk yakin da'akayi cikin Ramadana ba ko bayanai sosai gameda hakan, kawai munso bayyana wasu daga cikine kawai dan nuna muhimmancin wannan wata da tarihinsa wajen musulmi.

Thursday, May 1, 2008

Fatawa akan Azumi

TAMBAYA : Hadisin dayake cewa “ Kada kuyi Azumi ranar Asabar Face abinda aka Farlanta maku – wato Ramadan –“ shin Hadisin Ingantacce ne, kuma menene ma’anar Hadisin kuma shin ya kunshi dukkan Azumi ne?

ME BADA AMSA: Shaikh Abdur rahman bin Jibrin Mamba a cikin Majalisar manyan malamai masu fatawa a kasar Saudi Arabia.

AMSA: an kebance ranar Asabar ne da Hani saboda yahudawa sun kasance suna barin aiki a cikinta, se aka hana girmama ranar saboda kada ayi kamance – ceniya dasu, kuma ya halarta a Azumce Asabar idan akwai sababi, Kaman wanda yake Azumi rana ya sha ruwa rana, haka idan yayi dai- dai da ranar Arafa, ko Ranar Ashura da makamantansu, Ma’anar (abinda aka Farlanta maku) ma’anarsa aka shar’anta, kuma aka sunnanta maku.

Monday, December 31, 2007

Azumin Mara Lafiya

Musulunci Addini ne da ba bakauye ba , abin nufi Addini dayake tafiya da kowani irin zamani da kowani irin jama'a. saboda kaman yanda Allah Madauakakin Sarki yace (

Wednesday, November 21, 2007

ABUBUWAN DA'AKA HALASTA MA ME AZUMI

ABUBUWAN DA'AKA HALASTA MA ME AZUMI SUNE KAMAR HAKA:


1. Shiga cikin Ruwa da yin nitso aciki da sanyaya jiki saboda tsananin zafi, Domin Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance : ( "Yana zuba ruwa akansa, yana me Azumi saboda k�ishi ko saboda Zafi" Ahmad da Abu Dawud).

2. Yawayi gari yana me janaba ya halasta, Saboda fadin Nana A'isha Allah ya kara mata yarda :

( "Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yakasance yana wayan gari da janba yana Azumi sannan yayi wanka " Bukhari da muslim). wato acikin Azumin Ramadan.

3. Ci da Sha da Jima�i cikin dare har zuwa lakacin fitowar alfijir, Saboda fadin Ma�aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: ("Lallai Bilal yana kiran Sallah da dare, to kuci ku sha har se dan umm maktum ya kira sallah " Bukhari da muslim). Wato bilal nayin kira na farko shikuma yanayin kira na biyu.

4. Me jinin Haila da me jinin Bik'i, idan jinin ya yanke mata cikin dare ya halasta su jinkirta wankan har zuwa Asubahi, kuma su wayi gari da Azuminsu sannan suyi wanka kafin suyi Sallah.

5. Cin Aswaki a farkon Yini da karshensa, saboda cin Aswaki mustabbine kuma babu wani dalili da yanuna cewa za�ayi shi a wani lokaci banda wani, wannan shine mazhabin mafi yawan malamai.

6. Yin tafiya dan wata bukata ta halas koda tafiyan zatasahi shan ruwa.

7. Yin magani kowani Irii idan matukar baze tafi cikinsa ba kamar yin alluran da bata abinci bace.

8. Tauna abinci da d'and'ana shi da sharadin babu abinda zewuce ciki.

9. Yin amfani da turare da Shakan kanshi me dad'i.

Tuesday, November 20, 2007

KWANAKIN DA AZUMI YAKE HARAMUN A CIKINSU

KWANAKIN DA’AKA HARAMTA YIN AZUMI CIKINSU

1. Ranakun Idi guda biyu, Idi babba da Idi Krama, Saboda Fadin Umar dan khattab Allah yakara masa yarda: (“Lallai wadannan kwanaki guda biyu manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: yahana Azumi a cikinsu, Ranar da kuke shan daga Azuminku, da ranar da kuke ci daga yankanku” Muslim).
2. Kwanaki uku na shanyan nama (Ayyamut-tashreeq) wato kwanakin babban sallah guda uku, Sha daya da sha biyu da sha uku ga watan zulhijjah, Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wasallam: ya aiki Abdullahi dan Huzafah Allah yakara masa yarda yana kewayawa a muna yana cewa: (“kada kuyi Azumin wadannan kwanakin, domin su ranaku ne na cin da sha da ambaton Allah madaukakin sarki” Ahmad). Amma wannan banda mahajjaci, meyin tamattu’i da meyin Qiraani idan beda Hadaya.
3. Ranakun da mace take Haila da Bik’i, Saboda fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: a gameda hakkin mace, yace: (“Ba idan tayi haila bata sallah ba? To wannan shine tawaya -rashin cikan- addininta” Bukhari). Kuma malamai sunyi Ijma’i wato basuyi sabani ba akan bacin Azumin me haila da me bik’i.
4. Azumin mace idan mijinta na gari se idan ta nemi Izininsa, Saboda Fadin Ma’aiki Sallallahu Alaihi Wasallam: ( "Kada mace tayi Azumi alhali mijinta yana nan se dai idan da Izininsa amma banda Azumin ramadan" Bukhari da muslim).